Skip to main content



JIBWIS Ta Yi Allah Wadai Da Kashe-Kashen Da 'Yan Ta'adda Ke Yi A Yankin Arewa.


Kungiyar ta kuma umurci limaman juma'a da kamsul-salawat da suyi addu'oi a masallatai
Daga Ibrahim Baba Suleiman
Kungiyar wa'azin musulunci ta JIBWIS ta nuna alhininta da matukar damuwa akan kashe-kashen bayin Allah da basuji ba, basu gani ba da ake yi a Jihohin Katsina, Zamfara, Sokoto, Borno da sauran su.

Hakan ya fito ne daga bakin Shugaban JIBWIS Sheik (Dr) Abdullahi Bala Lau a wani zantawa da yayi da 'yan jaridu a maraicen asabar dinnan.

Shehin Malamin ya nuna damuwarsa matuka akan kisan kiyashi da ake yi a yankin arewa maso gabar, da arewa maso yamma, ''Ina mika sako na musanman ga Gwammatin tarayya cewa wannan kashe-kashen da ake yi fa yayi yawa, koda rai guda ne wajibine Gwannati ta kare ballantana rayukan mutane masu yawa.

Dole Gwamnati ta sake nazari domin tsare rayukan Jama'arta, tun mutane basu fara daukan makami domin kare kansu ba, wanda a karshe ana iya samun wata matsala idan mutane suka mallaki makamai a hannuwansu, Inji shi"
Shugaban na IZALA yaci gaba da cewa, Kiyaye rayukan mutane wajibine akan Gwamnati, domin da kiyaye rayuwar su ne za su ci gaba da yiwa Gwannati biyayya.

Ka'ida ce a cikin Al-Qur'ani, bayan Allah ya zaunar da Quraishawa lafiya kuma ya basu arziki sai ya ce musu:
ﻓﻠﻴﻌﺒﺪﻭﭐ ﺭﺏ ﻫﺬﺍ ﺍﻟﺒﻴﺖ
"Su bautawa Ubangijin wannan gida"
ﺍﻟﺬﻱ ﺃﻃﻌﻤﻬﻢ ﻣﻦ ﺟﻮﻉ ﻭﺀﺍﻣﻨﻬﻢ ﻣﻦ ﺧﻮﻑ *
"Wanda ya ciyar da su daga yunwa kuma ya amintar da su daga tsoro."

Saboda haka idan Allah zai bukaci Quraishawa su bauta masa saboda ya zaunar da su lafiya to, haka idan Gwamnati tana son 'yan kasarta su rika mata biyayya dari bisa dari, ta samar musu da zaman lafiya a garuruwan su.
Sheik Bala Lau ya ja hankalin Jami'an tsaro da su sani amanar 'Yan Nigeria ce Shugaban kasa ya saka su su wakilce shi, cin amana ne rashin tsayawa a kula da rayukan Jama'ah. Saboda haka wannan Kungiya ta IZALA tana kira da babban murya ga Jami'an tsaro da su kara daukan mataki domin tsare rayukan Jama'ah.
Daga karshen karshe, shugaban ya umurci Shugabannin JIBWIS na jihohi da kananan hukumomi musamman Malamai da Limamai a duk fadin Naijeriya da su lazimci addu'o'i akan Allah ya kawo mana karshen wadannan kashe kashen. Idan mu kayi wannan muna fatan zamu samu sauki daga Allah.

A karshe yace wannan Kungiya tana kara kira ga 'Yan Nigeria da su sani cewa babu abinda addu'a bata yi, mu dage da addu'a akan Allah ya zaunar damu lafiya, wadanda suka hada kai domin su yaki kasar nan Allah ya san su, Allah yayi mana maganinsu. Sannan mu yawaita tuba da Istigfari

Comments

Popular posts from this blog

TAJBank: Empowering Lives Through Non-Interest Banking

TAJBank: Empowering Lives Through Non-Interest Banking By Sani Ahmad Giwa   In a world where many financial institutions are driven by profit at the expense of their customers, TAJBank stands tall as a beacon of trust, integrity, and innovation. TAJBank is not just another bank — it is a movement toward ethical prosperity, financial inclusion, and peace of mind. If you’re searching for a banking partner that truly cares about your growth, your values, and your future — TAJBank is the answer. Why TAJBank? Because You Deserve Better Here’s why thousands of Nigerians across the country are making the switch to TAJBank: ✅ Non-Interest Banking (Riba-Free): TAJBank operates on Islamic finance principles, meaning no interest is charged or paid. Your money works for you in a way that’s ethical, fair, and transparent — without hidden fees or exploitative charges. ✅ Ethics First: At the core of TAJBank is a strong moral foundation. This is a bank that honors honesty, transparency, and mutual...
Tsaro: Za A Yi Zanga-Zanga A Arewacin Najeriya Kungiyar matasan Arewa karkashin jagorancin Alhaji Nastura Ahmad Shariff ta kira jama’ar arewacin Najeriya su fito suyi zanga zanga akan matsalar tsaro da ta addabi yankin a ranar Talata. Za a yi wannan zanga zanga ne a dukkanin jihohi goma sha tara na arewacin Najeriyar. Zanga zangar za ta kunshi kungiyoyin yan gwagwarmaya na farar hulla, kana za a watsa ta a kafafen sada zumunta. A baya bayan nan kuma dai harkar tsaro ta yi matukar gurbacewa a yankin Arewacin Najeriya musamman a jihohin Katsina, Sokoto da kuma Zamfara.
DOKAR FYADE: BA NAN GIZO KE SAKA BA Daga Sani Ahmad Giwa Fyade dai a Najeriya tun ba yau ba ya zama ruwan dare gauraye duniya, wanda kuma hukuma suka kasa daukan wani tsauraran matakai ga duk wanda ya aikata hakan akan kananan yara ko manya; inda lokuta da dama har wasu kungiyoyi ko masu hannu da shuni suke bai wa mutanen da suke aikata laifin fyade kariya ta hanyar daukar lauyoyi da makamantansu. Hakika wannan dabi'a ta sa guyawun iyayen yaran da aka lalata wa rayuwa yin sanyi wajen bin diddigin kwatar wa 'ya'yansu hakkinsu, haka suke hakura suna kai kokensu wajen Allah. Madallah da irin kokarin da majalisar dokokin kasa da na wasu jihohi suke yi na himmar samar da wata doka da za ta iya rage yawaitar wannan dabi'a ta fyade, kuma za ta tsoratar tare da razanar da masu sha'awar aikata hakan ga kananan yara ko manya. Kamar yadda yawancin membobin majalisar suka fi raja'a akan shi shi ne a zartas da hukuncin kisa ga duk wanda aka samu cikakkiyar shaid...