Skip to main content

DOKAR FYADE: BA NAN GIZO KE SAKA BA


Daga Sani Ahmad Giwa

Fyade dai a Najeriya tun ba yau ba ya zama ruwan dare gauraye duniya, wanda kuma hukuma suka kasa daukan wani tsauraran matakai ga duk wanda ya aikata hakan akan kananan yara ko manya; inda lokuta da dama har wasu kungiyoyi ko masu hannu da shuni suke bai wa mutanen da suke aikata laifin fyade kariya ta hanyar daukar lauyoyi da makamantansu.

Hakika wannan dabi'a ta sa guyawun iyayen yaran da aka lalata wa rayuwa yin sanyi wajen bin diddigin kwatar wa 'ya'yansu hakkinsu, haka suke hakura suna kai kokensu wajen Allah.

Madallah da irin kokarin da majalisar dokokin kasa da na wasu jihohi suke yi na himmar samar da wata doka da za ta iya rage yawaitar wannan dabi'a ta fyade, kuma za ta tsoratar tare da razanar da masu sha'awar aikata hakan ga kananan yara ko manya. Kamar yadda yawancin membobin majalisar suka fi raja'a akan shi shi ne a zartas da hukuncin kisa ga duk wanda aka samu cikakkiyar shaidar ya aikata fyaden.

Abun tambayar shi ne, shin dokar za ta yi tasiri bayan akwai sauran rina a kaba? Dalilin da ya sa na ce haka shi ne, mu dauki mas'alar Maryam Sanda wadda kotu ta yanke wa hukuncin kisa ta hanyar rataya, ina mai tabbatar muku ko da Appeal court ta sake yanke wa Maryam hukuncin kisa ba za a kashe ta ba, domin domin tana da damar sake daukaka kara zuwa kotun daga ita sai dai Allah ya isa, kuma ko a can din idan aka yanke mata hukuncin kisa ba za a kasheta ba, sai dai ta cigaba da zaman gidan yari har zuwa lokacin da gwamnatin Najeriya za ta gyara inda matsalar take.

Shin a ina matsalar take?

Babbar matsalar ko da an saka dokar kisa ga masu aikata fyade, sai gwamnatin Najeriya ta yi gyara a sashen ma'aikatan gidajen yari, kasancewar wadanda aka dauka domin zartar da hukuncin kisa ta hanyar rataya ko harbewa da bindiga yanzu duk sun mutu, sama da shekara ashirin da biyar har yanzu kuma gwamnati ba ta samar da wasu ba, ko kuma ba ta dauki ma'aikatan da za su dinga yin wannan aiki ba, kuma babu wanda yake da hakkin yin wannan kisa sai su. Saboda haka kafin waccan doka ya kamata a gyara inda matsalar take tukunna

Comments

Popular posts from this blog

TAJBank: Empowering Lives Through Non-Interest Banking

TAJBank: Empowering Lives Through Non-Interest Banking By Sani Ahmad Giwa   In a world where many financial institutions are driven by profit at the expense of their customers, TAJBank stands tall as a beacon of trust, integrity, and innovation. TAJBank is not just another bank — it is a movement toward ethical prosperity, financial inclusion, and peace of mind. If you’re searching for a banking partner that truly cares about your growth, your values, and your future — TAJBank is the answer. Why TAJBank? Because You Deserve Better Here’s why thousands of Nigerians across the country are making the switch to TAJBank: ✅ Non-Interest Banking (Riba-Free): TAJBank operates on Islamic finance principles, meaning no interest is charged or paid. Your money works for you in a way that’s ethical, fair, and transparent — without hidden fees or exploitative charges. ✅ Ethics First: At the core of TAJBank is a strong moral foundation. This is a bank that honors honesty, transparency, and mutual...
Tsaro: Za A Yi Zanga-Zanga A Arewacin Najeriya Kungiyar matasan Arewa karkashin jagorancin Alhaji Nastura Ahmad Shariff ta kira jama’ar arewacin Najeriya su fito suyi zanga zanga akan matsalar tsaro da ta addabi yankin a ranar Talata. Za a yi wannan zanga zanga ne a dukkanin jihohi goma sha tara na arewacin Najeriyar. Zanga zangar za ta kunshi kungiyoyin yan gwagwarmaya na farar hulla, kana za a watsa ta a kafafen sada zumunta. A baya bayan nan kuma dai harkar tsaro ta yi matukar gurbacewa a yankin Arewacin Najeriya musamman a jihohin Katsina, Sokoto da kuma Zamfara.